in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Keitany na fatan fafatawa a gasar Olympics ta birnin Rio
2016-01-04 15:17:33 cri
'Yar wasan tseren kasar Kenya, dake rike da kambin gasar gudun yada-kanin wani ta birnin New York Mary Keitany, ta bayyana fatan ta na shiga a fafata da ita, a gasar tseren Olympic ta birnin Rio wadda za a gudanar cikin watan Augusta mai zuwa.

Keitany wadda ta kuma zamo ta hudu a gasar Olympics a birnin London, gasar ta ta karshe kafin ta tafi hutun haihuwa na shekaru biyu, ta ce yanzu haka ta shirya tsaf domin tinkarar kalubalen da ke tafe a birnin Rio. 'yar wasan ta kuma kara da cewa, nasarar da take fatan samu a wannan karo, za ta zamo mai matukar muhimmanci gare ta, kasancewar sauran 'yan wasa daga kasar ta wato Kenya, su ma zasu yi duk mai yiwuwa don ganin sun lashe lambar zinari a gasar dake tafe.

A gasar birnin New York, Keitany ta kammala gudu cikin sa'oi 2:24:25, inda ta tserewa wacce ke biye da ita da minti daya da 'yan dakikoki.

Keitany mai shekaru 33 da haihuwa, na da kwarewa ta musamman a fagen tsere, ta kuma bayyana dalilan nasarar ta da suka hada da kwazo, da aiki tukuru, da basirar iya tsere da ta samu bayan tsahon lokaci.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China