in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin tana ci gaba da zama kasar dake sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arzikin duniya
2016-01-04 13:55:58 cri
A kwanakin baya ne cibiyar nazarin tattalin arziki ta kasa da kasa ta kwalejin kimiyyar zamantakewar al'umma da ke birnin Shanghai na kasar Sin ta gabatar da rahoton nazarin tattalin arzikin duniya na shekarar 2016, inda ta yi nunin cewa, a shekarar 2016, tattalin arzikin duniya zai farfado sannu a hankali.

Sabbin bangarori biyar da Sin ta inganta a sabon tsarinta na yau da kullum na tattalin arziki suna bayar da gudummawa wajen bunkasa tattalin arzikin duniya, kuma Sin ta ci gaba da zama kasar dake sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arzikin duniya.

Rahoton ya yi hasashen cewa, bunkasuwar tattalin arzikin duniya a shekarar 2015 ya kai kashi 3 cikin dari,kana a shekarar 2016 zai kai kashi 3.24 cikin dari, yayin da a shekarar 2017 zai kai kashi 3.43 cikin dari, wadanda ya yi kasa da zaton da aka yi a shekarar bara.

A bangaren kasar Sin kuwa, rahoton ya yi nuni da cewa, a shekarar da ta gabata, ko da yake saurin bunkasuwar tattalin arzikin kasar ya dan ragu amma ya bunkasa cikin sauri. Ana kuma ci gaba kokarin kyautata tsari da tabbatar da ingancin bunkasuwar tattalin arziki yadda ya kamata. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China