in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Nijeriya za ta soke rangwamen man fetur a farkon shekarar 2016
2015-12-26 13:54:05 cri
Ministan harkokin man fetur na kasar Nijeriya Ike Kachikwu ya bayyana a ranar Jumma'a 25 ga wata cewa, gwamnatin kasar za ta soke rangwamen man fetur tun ranar 1 ga watan Janairu na shekarar 2016 mai zuwa.

A yayin da ministan ke ziyarar aiki a garin Fatakwal na jihar Rivers da aka fi sani da rinjaye wajen fitar da man fetur na kasar Nijeriya, ya bayyana cewa, a halin yanzu, gwamnatin ba ta iya biyan rangwamen man fetur , shi ya sa, za ta soke rangwamen tun daga farkon shekarar 2016.

Kasar Nijeriya ita ce babbar kasar da ke fitar da man fetur a nahiyar Afirka, amma sabo da ba ta iya tace danyen mai sosai, shi ya sa, take sayo galibin man fetur daga kasashen ketare, lamarin da ya sa ake gamuwa da karancin man fetur a kasar a kullum. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China