in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan mutanen da suka rasa rayukan su sakamakon bala'in guguwa a nan kasar Sin ya kai 17
2014-07-20 16:51:55 cri
Rahotanni daga kudancin kasar Sin sun ce ya zuwa Lahadin nan, yawan mutanen da suka rasu sakamakon mahaukaciyar guguwar da aka yiwa lakabi da Rammasun ya kai mutum 17, bayan da aka samu karin mutum 1 da ya rasa ransa sakamakon hakan a tsibirin Hainan.

Guguwar dai ta Rammasun wadda ba a taba ganin irin ta a yankin na kudancin kasar Sin cikin shekaru 40 da suka wuce ba, na tafe da iska mai karfi da ruwa kamar da bakin kwarya, ta kuma kutsa wasu yankuna na lardunan dake kudancin kasar.

Mahukuntan kasar Sin sun ce baya ga wadanda suka rasu, akwai kuma wasu mutane 2 da suka bace sakamakon wannan bala'i.

Alkaluman baya bayan nan dai sun shaida cewa, bala'in guguwar ya ritsa da al'umma fiye da miliyan 5, yayin da guguwar ke ci gaba da barna a wasu karin yankunan dake bakin teku, ciki hadda wadanda ke lardunan Guangdong, Hainan, da kuma jihar Guangxi mai cin gashin kanta.

Yanzu haka, an tabbatar da mutuwar mutane 8, ciki har da jami'ai masu kula da aikin ceto 2 a lardin Hainan, sai kuma sauran mutane 9 daga lardin Guangxi. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China