in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU za ta tura tawagar masu sa ido a zaben jamhuriyar Afrika ta tsakiya
2015-12-19 13:44:15 cri
Shugaban kwamitin kungiyar tarayyar kasashen Afrika AU, Madam Nkosazana Dlamini-Zuma ta amince da aika tawagar wucin gadi don sa ido a babban zaben kasar jamhuriyar Afrika ta tsakiya da za'a yi a ranar 27 ga watan na Disamba,

Tawagar wucin gadin wanda za'a tura sakamakon gayyatar da gwamnatin kasar ta yi za ta isa birnin Bangui ne a ranar 20 ga wata kuma za ta kasasnce a cikin kasar har zuwa 30 ga wata, a bayanin da kungiyar AU ta fitar a jiya Jumma'a.

Tawagar sa ido a zabe na kungiyar AU zai kasance karkashin jagorancin Souleymane Ndene Ndiaye, tsohon Firaministan kasar Saliyo inji sanarwar.

Za'a tura jami'an sa idon a dukkan gundumomin zaben kasar domin lura da yadda za'a tafiyar da zaben da kuma tattaunawa da manyan masu ruwa da tsaki a cikin ayyukan zaben inji sanarwar AUn. (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China