in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Kenya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar ba da tallafi
2015-12-18 10:53:48 cri

Gwamnatocin kasashen Sin da Kenya sun sanya hannu kan wasu yarjejeniyoyi 3 kan wasu ayyukan tallafi a kasar Kenya, wacce ke gabashin Afrika.

Ayyukan 3 wadanda aka ware kudi kimanin dalar Amurka miliyan 152.4 kuma an sanya hannu kan yarjejeniyar ne a ranar Larabar nan a Nairobi, tsakanin sakataren ma'aikatar adana kudaden kasar Kenya Henry Rotich, da ministan kasuwancin kasar Sin Gao Hucheng.

A yayin bikin sanya hannun, shugaba Kenyatta, ya bayyana bukatar hadin kan Sin da Kenya domin sanya ido kan yadda za'a aiwatar da ayyukan raya ci gaban Afrika, wanda aka ambata a yayin taron hadin gwiwar Sin da Afrika wato FOCAC.

A nasa bangaren, Gao Hucheng ya ce, bayan tallafawa Kenya a fannin makamashi da kayayyakin more rayuwa da aikin gona da ilmi da lafiya, haka zalika kasar Sin, tana tallafawa Kenya wajen ci gaban fannin gandun daji.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China