in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 11 sun halaka a wani harin kunar bakin wake a yankin arewa mai nisa na kasar Kamaru
2015-12-11 20:15:07 cri
Rahotanni daga Younde na kasar Kamaru ya tabbatar da cewar mutane a kalla 11 ne suka halaka sannan wassu da dama suka ji rauni a safiyar Jumma'an nan a yankin arewa mai nisa na kasar Kamaru, sakamakon wani harin kunar bakin wake da aka kaddamar, kamar yadda wata majiyar soji ta tabbatar.

Majiyar ta ce wata yarinya ce mai shekaru kusan 13 ta afka wani gida a Kolofata, wani gari dake makwabtaka da Nigeriya da kusan karfe 6 na safe agogon kasar kafin ta kwance bam din dake jikin ta, abin da ya hallaka kanta da wadansu guda 5, da dama kuma suka ji rauni.

Majiyar ta ce daga cikin mutanen da suka mumman rauni guda 5 suka sake mutuwa a asibiti abin da ya kawo adadin wadanda suka mutu zuwa kusan 11.

Har yanzu dai babu wata kungiyar da ta dauki alhakin harin.(Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China