in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Najeriya ta rage tarar da ta ci kamfanin MTN
2015-12-04 10:20:12 cri

Hukumar da ke sanya ido kan kamfanonin sadarwa a Najeriya, ta ce ta rage tarar dala biliyan 5.2 da ta ci kamfanin sadarwa na MTN.

Kamfanin na MTN ya bayyana cikin wata sanarwa da ya fitar a jiya cewa, hukumar ta rage tarar ce bayan wasu tattaunawa da hukumomin kasar.

Hukumomin Najeriyar dai sun ci kamfanin na MTN tarar ce, saboda ya gaza rufe layuka miliyan 5.1 a watannin Agusta da Satumba saboda ba su da rijista.

Yanzu dai kamfanin na MTN zai biya tarar dala biliyan 3.4 ne kafin ranar 31 ga watan Disamba(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China