in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Faransa ta shirya zaman makoki ga wadanda suka mutu a hare-haren ta'addanci da aka kai kwanan baya
2015-11-28 12:49:09 cri
A jiya 27 ga wata, gwamnatin kasar Faransa ta shirya wa mutane 130 wadanda suka mutu a jerin hare-haren ta'addanci da aka kai yau da makonni biyu da suka gabata gagarumin zaman makoki a filin Otel des Invalides dake cikin birnin Paris.

A yayin zaman, shugaba François Hollande na kasar Faransa ya yi wani jawabi, inda ya ce, ranar 13 ga watan Nuwamba rana ce da ba za su manta da ita ba har abada. A wancan rana, an dauki mugun matakin kai hare-hare kan birnin Paris. A cikin wadannan hare-haren da aka shirya a ketare, wasu masu laifin kisan gilla sun hallaka 'yan uwansu 130 tare da wasu daruruwa suka jikkata. Ya ce, dukkan 'yan Faransa suna makokin wadanda aka hallaka.

A yayin zaman makokin, a kan wani babban na'urar bidiyo, an nuna hotunan wadanda aka hallaka su a cikin harin daki daki.

Kafofin talibijin na kasar Faransa da wasu muhimman kafofin talibijin na kasa da kasa sun yada labaru game da zaman makokin kai tsaye. Mutane kimanin dubu 2, ciki har da firaministan gwamnatin Faransa da shugabannin majalisun dokokin kasar da ministocin gwamnati da wakilan jam'iyyun siyasa da sojojin rundunar ko ta kwana da wasu likitoci da nas-nas da dukkan iyalan wadanda suka mutu ko suka jikkata cikin harin sun halarci makokin. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China