in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An hakikance mutanen nan 103 da suka rasa rayukan su a harin ta'addaci a Paris
2015-11-16 10:53:36 cri
Firaministan kasar Faransa Manuel Valls, ya sanar a Lahadin nan cewa, a yanzu haka, an tabbatar da asalin mutanen nan 103 cikin wadanda suka rasa rayuka sakamakon harin nan na birnin Paris. Cikin mutanen da suka mutu, baya ga 'yan asalin kasar Faransar, har ma da 'yan asalin kasashen Birtaniya, Spainiya, Portugal, Belgium, Switzerland, Aljeriya, Morocco, Tunisia, Chile, Mexico da dai sauransu.

A nashi bangaren, ministan harkokin cikin gidan kasar Faransa, mista Bernard Cazeneuve ya fada cewar, an tsara kan harin ne a kasashen waje, yayin da wasu mutanen dake cikin kasar ta Faransa suka tallafawa shirin. A halin yanzu, 'yan sandan kasashen Faransa da Belgium dake bincike kan musabbabin faruwar lamarin, suna kara samun ci gaba. 'Yan sandan kasar Faransa sun gabatar da wata sanarwa a ranar Lahadin nan, inda ake kira ga jama'a da su taimaka wajen yunkurin neman Abdeslam Salah, wanda ake zarginsa da hannu a harin na Paris, kafin haka kuma 'yan sandan Belgium ne suka sanar da cigiyar tasa.

A nasu bangare, masu kula da aikin shigar da kararraki na birnin Paris, sun tabbatar da cewa, Ismail Omar Mustafa wanda aka haifa a kasar Faransa a shekarar 1985, na daga cikin mutanen da ake zargi da hannu a kai harin, kuma a halin da ake ciki, tuni 'yan sanda sun tsare mutane 7 daga cikin dangin sa.

Ban da haka kuma, akwai labarin da ya nuna cewa, wasu mutane 3 daga cikin masu kai hare-haren a Paris sun kasance 'yan uwan juna. Cikinsu daya ya mutu, dayan ma an kama shi a Belgium, yayin da na 3 har yanzu ba a san inda yake ba.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China