in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin MDD ya damu da karuwar ayyukan 'yan fashin teku a gabar ruwan Somaliya
2015-11-27 09:41:25 cri

Wakilin musamman na babban magatakardan MDD Nicholas Kay ya yi Allah-wadai da yadda wasu 'yan fashen teku suka yi awon gaba da jirgin ruwan kamun kifi na kasar Pakistan a gabar ruwan Somaliya.

Mr Kay ya ce, ya damu matuka kan yadda ake samun karuwar ayyukan 'yan fashin teku a 'yan kwanakin nan a shiyyar, bayan da aka samu nasarar kawar da matsalar shekaru uku da suka gabata.

Ya ce, wannan matsala na iya gurgunta irin ci gaban da kasar ta Somaliya ta samu bayan farfadowa daga yakin basasa na tsawon shekaru ashirin.

Don haka, Mr Kay ya yi kira ga masu jiragen kamun kifi da su mutunta dokokin kamun kifi na gwamnatin tarayyar Somaliya, sannan su martaba shiyyar cinikayyar kasar da aka kebe.(Ibarhim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China