in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin tsaron MDD ya yi suka kan sabon harin da aka kai a Somaliya
2014-05-05 09:58:02 cri

Kwamitin tsaro na MDD a ranar Lahadin nan 4 ga wata ya yi kakkausar suka a kan mummunan harin da aka kai na bam a Mogadishu, babban birnin kasar Somaliya, yana mai kiran shi da na ta'addanci, sannan ya jaddada goyon bayansa ga bukatar samar da zaman lafiya da tattaunawar sulhu a kasar.

Mambobin kwamitin sun yi suka a kan harin da kungiyar Al-Shabaab ta dauki alhakin aiwatarwa, abin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama, wassu kuma suka samu raunuka, kamar yadda wata sanarwa da kwamitin mai wakilai 15 ya fitar.

A bisa ga bayanai da aka fito, wani bam ne da aka ajiye a gefen titi mai cike da jama'a ya tarwatse a Mogadishu a ranar Asabar, wanda nan take ya hallaka mutane 6, wassu guda 7 kuma suka ji rauni.

Kungiyar masu tsattsauran ra'ayin addinin islama Al-Shabaab ta sanar da kai wannan harin domin ta samu motar wani tsohon jami'in gwamnati da ke wucewa a daidai wannan lokaci wanda shi ma ya hallaka a cikin harin. (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China