Kasar Zimbabwe na nuna yabo da zuba jarin kasar Sin, tare da fatan kara fadada dangantakar tattalin arziki da kasuwanci tare da kasar Sin, in ji ministan gwamnatin kasar, kafin zuwan shugaban kasar Sin Xi Jinping wannan kasa a mako mai zuwa.
Bisa neman muradun ci gaban kasa, Zimbabwe na yabawa da jarin da kasar Sin ta zuba, in ji ministan masana'antu da kasuwanci, Mike Bimba, a yayin wani dandalin zuba jari tsakanin Zimbabwe da kasar Sin da aka shirya a birnin Harare. (Maman Ada)