in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta ba da kudin tallafi ga shirin WFP don taimakawa jama'ar kasar Sudan ta kudu
2015-11-25 16:20:04 cri

Shirin kula da harkokin abinci ta MDD (WFP), ya karbi kudin tallafin da gwamnatin Sin ta samar domin tinkarar matsalar karanci abinci a kasar Sudan ta kudu.

Wakilan shirin sun ce sun karbi dalar Amurka miliyan 5, kudaden da za a yi amfani da su wajen sayen hatsi, da wake, da mai, da kuma gishiri domin taimakawa wadanda matsalar ta fi shafa a yankunan kasar Sudan ta kudu. An dai kiyasta cewa, mutane miliyan 3 da dubu dari 9 ne a Sudan ta kudun ke fuskantar karancin abinci.

Jami'i mai kula da harkokin da suka shafi kasar Sudan ta kudu na shirin WFP ya bayyana cewa, taimakon na Sin zai biya bukatun dunbin mutanen dake fama da karancin abinci a kasar. (Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China