in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An sake bude makarantu a Bornon Najeriya duk da fargabar tabarbarewar tsaro
2015-11-25 10:36:34 cri

An sake bude makarantu a jahar Borno dake arewacin Najeriya a ranar Talatar nan, bayan shafe sama da shekara guda makarantun na rufe sakamakon hare haren kungiyar Boko Haram.

Kafin sake bude makarantun dai, gwamnatin jihar Borno ta bukaci iyayen yara su tura 'yayan su makarantun, duk da irin fargabar dake zukatan al'umma na yawaitar hare hare daga kungiyar mai ikirarin kishin Islama.

Musa Kubo, kwamishinan ilmin jihar Borno ya ce, akwai tabbaci dangane da samar da tsaro a makarantun jihar.

A tsawon lokutan da makarantun jihar suka kasance a rufe, an yi amfani da su ne wajen ba da mafaka ga mutanen da hare haren Boko Haram suka daidaita.(Ahmed Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China