Magatakardar MDD Ban Ki-moon ya soki kisan da aka yi wa ma'aikacin wanzar da zaman lafiya a jamhuriyar Afrika ta Tsakiya CAR a jiya Talata, tare da bukatar a binciko a kuma gurfanar da wadanda ke da hannu a gaban shari'a.
Magatakardar ya soki kisan ne na ma'aikacin dake aiki a ofishin majalissar ta MINUSCA, a garin Batangafo mai tazaran kilomita 400 daga arewacin Bangui, babban birnin kasar, in ji sanarwar da kakakinsa ya fitar wa manema labarai.(Fatimah)