in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude taron tattalin arzikin Afrika karo na 10 a DRC
2015-11-03 10:25:13 cri

Shugaban majalisar dattawan jamhuriyar demokuradiyar Congo DRC Leon Kengo Wa Dondo ya bude taron tattalin arzikin Afrika (AEC) karo na goma a ranar Litinin a birnin Kinshasa, wanda kuma a wannan shekara aka dora muhimmanci kan yaki da talauci da bambance bambance a nahiyar Afrika.

Taken taron na wannan karo, shi ne "Yaki da talauci da bambance bambance a cikin shirin bunkasuwa na bayan shekarar 2015".

Taron dake gudana tun daga ranar 2 zuwa 4 ga watan Nuwamba, ya samu halartar masu fada a ji, kwararru a fannin ci gaba da kuma masana, inda suke tattauna hanyoyin da za a bi domin kawar da talauci, da kuma yadda za'a magance bambance bambance a nahiyar Afrika a cikin tsarin sabbin maradun duniya na yaki da talauci. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China