in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
DRC da Rwanda sun dauki niyyar karfafa tsaro da murkushe 'yan tawayen FDLR
2015-09-25 10:16:33 cri

Jamhuriyar demokaradiyyar Congo (DRC-Congo) da kasar Rwanda sun bayyana niyyarsu ta murkushe dakarun kungiyar 'yan tawayen dake kokarin tabbatar da demokaridiyya da kwato 'yancin Rwanda (FDLR) dake gudanar da ayyukanta a gabashin DRC-Congo, a cewar wata sanarwar da aka fitar bayan wani zaman taron ministocin tsaro na kasashen biyu da ya gudana a ranakun Labara da Alhamis a birnin Kigali, hedkwatar kasar Rwanda.

Taron ya baiwa ministan tsaron Rwanda James Kabarebe da ministan tsaron Congo Aime Ngoi-Mukena, damar tattauna kalubalolin tsaro da kasashen biyu suke fuskanta, in ji wannan sanarwa. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China