in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gudanar da zaben shugaban kasa a Cote d'Ivoire lami lafiya, in ji MDD
2015-10-27 10:00:10 cri

Tawagar jami'an aikin wanzar da zaman lafiya ta MDD a Cote d'ivoire UNOCI ta ce, an gudanar da zaben shugaban kasar a ranar Lahadin da ta gabata ba tare da tashin hankali ba.

Yan takara 10 ne suka tsaya a zaben, ciki har da shugaban kasar mai ci Alassane Ouattara, kuma ana sa ran zaben zai kawo karshen tashin hankalin da ya gurgunta kasar sakamakon rikicin bayan zabe da ya barke a kasar tsakanin shekarar 2010 zuwa 2011 bayan zaben shugaban kasar a wancan lokaci.

Mai magana da yawun babban sakataren MDD Stephane Dujarric, ya ce, ana sa ran bayyana alkaluman farko na sakamkon zabe a yau ko gobe Laraba.

Dujarric ya ce, jami'an UNOCI suna taimakawa jami'an 'yan sandar kasar da sojoji da sauran jami'an tsaro a kasar domin tabbatar da tsaro a kasar.

Ya ce, MDD ta tanadi jiragen sama na ko ta kwana da sauran ababan sufuri domin jigilar muhimman kayyakin zaben zuwa birnin Abidjan.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China