in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a gudanar da kuri'ar jin ra'ayin jama'a a yankin Darfur a shekara mai zuwa
2015-10-19 20:43:36 cri
Shugaba Omar al-Bashir na Sudan ya bayyana cewa, za a gudanar da kuri'ar jin ra'ayin jama'a game da yankin Darfur a watan Afrilun shekara mai zuwa.

Shugaba Al-Bashir wanda ya bayyana hakan a yau yayin bude zaman majalisar dokokin kasar na biyu, ya ce, matakin zai taikawa wajen kawo karshen matsayin yankin ta fuskantar tafiyar da harkokin mulki.

Shugaba na Sudan ya kuma lashi takwabin tabbatar da zaman lafiya a yankin Darfur da ragowar sassan kasar tare da tabbatar da cewa, mutanen da suka bar gidajensu sun koma matsugunansu.

Tun a shekarar 2003 ne yankin Darfur ke fuskantar yakin basasa. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China