in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta bukaci bangarorin dake rikici da juna a Sudan ta kudu da su cika alkawarin tsagaita bude wuta
2015-10-10 10:56:53 cri
Zaunannen wakilin Sin a M.D.D. Liu Jieyi ya fada a jiya Jumma'a cewa, don tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Sudan ta Kudu, yanzu haka, babban aikin da ke gaban su shi ne goyon bayan kokarin kungiyar AU da kungiyar samun ci gabar gwamnatocin kasashen gabashin Afrika wato IGAD, don ganin bangarorin dake rikici a Sudan ta Kudu sun cika alkawarin da suka dauka na tsagaita bude wuta.

A wannan rana, kwamintin sulhu na M.D.D. ya zartas da shiri mai lamba 2241 da kuri'un amincewa 13, kana da kuri'un kauracewa 2, don kara wa'adin aikin wanzar da zaman lafiya ga tawagar musamman ta M.D.D. zuwa Sudan ta Kudu, inda Sin ta jefa kuri'ar amincewa.

Liu Jieyi ya ce, Sin ta yabawa M.D.D. kan kokarin da ta yi wajen yin taka tsan-tsan game da saka takunkumi ga Sudan ta Kudu.

Liu Jieyi, yayi fatar cewar matakan da kwamitin sulhu na M.D.D. ya dauka zai yi tasiri a yunkurin samar da zaman lafiya da kawo karshen rikicin a Sudan ta kudu.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China