in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dandali kan tasirin El Nino a gabashin Afrika zai gudana a Kenya
2015-10-19 10:50:14 cri

Kasashen gabashin Afrika za su shirya a birnin Naivasha na kasar Kenya, wani taron tuntubar juna na shiyya kan tasirin El Nino da kuma shirye shiryen ayyukan yin rigakafi a ranar Talata mai zuwa.

Kungiyar raya gwamnatocin gabashin Afirka ta IGAD ta jaddada cewa, shirya taron daga ranar 20 zuwa 21 ga watan Oktoba na da manufar fadakar da kasashe kan illolin El Nino.

Masu shirya taron na fatan yin amfani da dandalin tuntubar juna domin taimakawa kwararrun kasashe da na shiyyoyi wajen fadakar da jama'a da samar da bayanai na baya baya kan El Nino, har ma da shirye shirye a bangaren al'ummomin na dukkan shiyyar, in ji kungiyar IGAD a cikin wata sanarwa a birnin Nairobi.

Taron na tuntubar juna zai taimaka wajen hada masanan yanayi, kwararru a fannin sadarwa, masu fada a ji a fannin siyasa, da ma ministocin kudi, da ministocin dake kula da haduran bala'u na kusurwar Afrika.

Wasu kungiyoyin ba da agaji sun yi gargadin cewa, shiyyar kasashen Afrika dake kudu da hamadar Sahara za ta iya fuskantar barazanar yunwa, tare da ruguwar albarkatun noma bisa tasirin El Nino. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China