in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Najeriya sun lashi takwabin kawo karshen ayyukan ta'addanci a kasar kafin watan Disamba
2015-10-05 13:29:37 cri
Dakarun Najeriya sun lashi takwabin kawar da ayyukan ta'addanci a kasar ko ta halin kaka kafin watan Disamba.

Kwamandan sojojin da ke kula ayyukan yaki da mayakan Boko Haram a garin Maiduguri da ke yankin arewa maso gabashin kasar Manjo Janar Yusha'u Abubakar ne ya bayyana hakan a lokacin da ya ke bayani game da hare-haren kunar bakin wake na baya-bayan da aka kai a sassan kasar, hare-haren da ya ce, an kai su ne da nufin janye hankulan sojojin kasar daga irin nasarorin da suke samu a yakin da suke yi da 'yan ta'adda.

Kwamandan ya ce, babu abin da zai hana sojojin ganin bayan ayyukan ta'addanci a kasar kafin watan Disamba. Ya ce, tuni sojojin suka samu wasu bayanan sirri game da wadannan ke da hannu a hare-haren bama-baman da aka kai a birnin Maidugurui, fadar mulkin jihar Borno. Kuma yanzu haka ana ci gaba da gudanar da bincike.

Don haka ya yi kira ga 'yan Najeriya, da su ci gaba da baiwa jami'an tsaro hadin kai don hana aukuwar hakan nan gaba. Ya kuma bayyana cewa, sojojin na kokarin bullo da dabarun da suka dace ta yadda jama'a za su rika baiwa hukumomin tsaro muhimman bayanai ba tare da kowa ya sani ba.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China