in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Matakan gudummawa da shugaban Sin Xi Jinping ya gabatar a MDD sun bayyana manufar neman makomar dan adam ta bai daya
2015-10-04 14:22:06 cri
Game da matakan gudummawa da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar yayin da yake halartar tarurukan tunawa da cika shekaru 70 da kafa MDD a kwanakin baya, shugaban sashen kula da bada taimako ga kasashen waje na ma'aikatar harkokin cinikayya ta kasar Sin ya yi wani jawabi a ranar 3 ga wata cewa, matakan sun bayyana niyyar gwamnatin kasar Sin da ta jama'arta ta yin kokari tare da kasashe masu tasowa da jama'arsu wajen neman samun ci gaba cikin adalci.

Wannan jami'i ya bayyana cewa, shugaba Xi Jinping ya halarci tarurukan tunawa da cika shekaru 70 da kafa MDD da taron kula da hadin gwiwa a tsakanin kasashe masu tasowa da kuma taron koli na mata a karshen watan Satumba, tare da sanar da wasu matakai a gun wadannan taruruka, wadanda kuma suka shafi fannoni biyar, kamar Sin za ta kafa asusun raya hadin gwiwa a tsakanin kasashe masu tasowa, wanda a mataki na farko, za a samar da kudi dala biliyan 2 don nuna goyon baya ga kasashe masu tasowa wajen aiwatar da ajendar samun bunkasuwa bayan shekarar 2015.

Hakazalika kuma, jami'in ya bayyana cewa, ma'aikatar harkokin cinikayya ta kasar Sin da hukumomin da abin ya shafa za su yi nazari tare da daukar matakai bisa bukatun kasashen da za su karbi taimakon, don cika alkawarin Sin na samar da gudummawa yadda ya kamata. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China