A yayin wata zanga zangar adawa da ya shirya, kawancen CNC ya bayyana cewa ba zai halarci zabuka tare da shugban hukumar zabe mai zaman kanta na yanzu ba.
Dokar kasa ta nuna cewa, shugaban hukumar zabe ana zaben shi bisa tsawon shekaru shida kawai, ba wai a kara sake zabensa ba. Youssouf Bakayoko ya yi shekaru shida, sun isa, ba za a sake zabensa ba, in ji Martele Mamadou Koulibaly, kakakin kawancen CNC.
A cewar mista Koulibaly, cigaba da kasancewar mista Bakayoko a kan mukaminsa, take doka ne da kuma kundin tsarin mulki. Dole ne mista Bakayoko ya yi murabus, in ji kakakin CNC.
'Yan Cote d'Ivoire na shirye shiryen zuwa zabuka a ranar 25 ga watan Oktoba mai zuwa, tare da 'yan takarar shugaban kasa goma, wanda ya hada da shugaban kasar mai ci na yanzu Alassane Ouattara.
Kawancen CNC dake kunshe da 'yan takarar shugaban kasa hudu, ya shirya wata zanga zanga domin ganin an daidaita kamfen a kafofin watsa labarai na gwamnati cikin adalci da kwarewa da kuma kawo gyaran fuska ga hukumar zabe. (Maman Ada)