in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi kira da a kwantar da hankali bayan fada kan iyaka tsakanin DRC da Rwanda
2014-06-13 10:20:33 cri

Martin Kobler, shugaban tawagar MDD MUNUSCO a jamhuriyar demokradiyya ta Congo DRC, ya roki jama'a da su kwantar da hankulansu, musamman bayan fadan kan iyaka da aka gwabza tsakanin sojojin Congo da na Rwanda.

Kakakin MDD Farhan Haq ya bayyana wa wani taron manema labarai cewar, Kobler na ci gaba da tuntubar hukumomin Congo da na Rwanda, a kokarin da ake yi na kashe wutar rikicin, tare da sanya Rwanda da jamhuriyar demokradiyyar Congo, a kan turba aiwatar da tsarin hadin kai, na wanzar da zaman lafiya da tsaro, da kuma ci gaba da zama makwabtan juna na gari.

Sojojin Rwanda da na Congo sun yi fada da juna a cikin kwanaki biyu, a kan iyaka a ranar Alhamis, rahotanni na cewar, tashin hankalin na barazanar rikidewa zuwa yaki da juna. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China