in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kammala taron G77 da Sin a Bolivia
2014-06-16 20:57:54 cri
A jiya Lahadi ne aka kammala taron kolin kungiyar kasashen G77 da kasar Sin a Santa Cruz da ke gabashin kasar Bolivia, inda aka amince da wata yarjejeniyar bullo da wata sabuwar dokar kasa da kasa da za ta kai ga samar da duniya mai zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Taron na yini biyu, ya kuma zo dai-dai da cikon shekaru 50 da kafa kungiyar ta G77 wadda ke da mambobin kasashe masu tasowa 133.

Mataimakin shugaban kwamitin majalisar wakilan jama'ar Sin Chen Zhu ya halarci taron a matsayin manzon musamman na shugaba Xi Jinping na Sin.

Chen ya bayyana kudurin Sin na kara karfafa hadin gwiwa da kungiyar ta yadda za a bunkasa ci gaba da makomarta. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China