in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta bukaci kokarin kasashen G77 a kan sabuwar hanyar dangantaka ta kasa da kasa
2015-01-09 19:09:15 cri
Manzon kasar Sin a ranar alhamis din nan ya yi kira ga kasashen G77 dasu inganta kokari na samar da sabuwar hanyar dangantaka da zai samar da moriya ga kowane bangare tun daga tushe.

Liu Jieyi, wakilin kasar Sin na din din din a MDD ya bubakci hakan a wani bikin majalissar da aka yi a cibiyar nan a birnin New York, inda Kasar Bolivia ta mika ragamar jagorancin kungiyar G77 ga kasar Afrika ta kudu.

Mr Liu yace akwai tabbacin cewa karkashin jagorancin kasar Afrika ta kudu, kungiyar ta G77 tare da kasar Sin zasu cigaba da al'ada mai kyau na goyon bayan juna da hadin gwiwa sannan kuma zasu cigaba da ganin ana samar da cigaba a kasashe masu tasowa tare.

Wakilin yace a matsayinta na daya daga cikin kasashe masu tasowa, Kasar Sin tana mutunta ayyukan kungiyar ta G77 matuka da kuma hadin gwiwar ta tare da kasar Sin.

Wannan kungiyar itace mafi girma ta kasashe masu tasowa a tsakanin gwamnatocinsu, wadda ke da zummar inganta tattalin arzikin da samar da daidaito a cikin al'ummomin kasa da kasa. Fatimah

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China