Rundunar 'yan sandan Najeriya ta bayyana cewa, ta kama mutane 56 a yankin tsakiyar kasar wadanda ake zaton 'yan kungiyar Boko Haram ne.
Kwamishinan 'yan sandan jihar Kogi Emmanuel Ojukwu ya shaidawa manema labarai a Lokoja, fadar mulkin jihar cewa, an damke wadanda ake zargin ne a maboyarsu daban-daban da ke kauyen Obajana da ke wajen birnin Lokoja.
Ojukwu ya ce, 'yan sandan sun kaddamar da samamen ne, sakamakon wani hari da aka kaiwa motar sintirin 'yan sandan a kauyen Obanaja a ranar 14 ga watan Satumba wanda ya yi sanadiyar halaka wani sipeton 'yan sanda.
Kwamishinan ya ce, 'yan sandan sun yi nasarar kwato muggan makamai da kwayoyin sa maye a yayin wannan samame, kuma nan ba da dadewa ba za a gurfanar da wadanda ake zargi a gaban kotu.(Ibrahim)