in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babbar jam'iyyar adawa a Mozambique za ta dau fansar hari da aka kaiwa shugabanta
2015-09-18 10:38:47 cri

Babbar jamiyyar adawar kasar Mozambique Renamo ta ce za ta dau fansa na yunkurin hallaka shugabanta Afonso Dhlakama, amma ta ce za ta dau matakin ne a siyasance.

Rahotanni sun ce, Dhlakama ya sha da kyar, bayan samun raunuka da ya yi a lokacin da 'yan bindiga suka budewa tagawar sa wuta a daren Asabar din da ta gabata a taskiyar lardin Manica, sannan harin ya raunata magoya bayan jamiyyar ta Renamo 4.

Jam'iyyar ta Renamo, ta zargi gwamnati da daukar nauyin harin, zargin da babbar jamiyyar kasar Frelimo ta musanta.

A yayin gudanar da taron manema labarai a ranar Alhamis din nan, babban sakataren jam'iyyar ta Renamo Manuel Bissopo ya bayyana cewar, jam'iyyar za ta dau fansa kan harin da aka kai mata, ya kara da cewar, ba za su laminci irin wannan ta'addanci ba.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China