Shugaban kasar Aljeriya Abdelaziz Bouteflika, ya sauke Manjo Janar Mohamed Mediene, shugaban hukumar leken asirin ta DRS daga mukaminsa.
Rahotanni sun ce, shugaba Bouteflika ya kuma maye gurbin Mediene da Mr. Othmane Tatag, wanda kafin nadinsa daya ne daga mashawartan shugaban kasar, ya kuma taba aiki a hukumar leken asirin kasar.
A cewar shugaban jam'iyyar FLN mai mulkin kasar Amar Saadani, shugaban na Aljeriya na gudanar da ire-iren wadannan sauye sauye kan rundunonin soji, da sauran jami'an tsaron kasar ne, a wani mataki na aiwatar da gyaran fuska ga tsarin gudanar da mulki.(Saminu)