in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin kasa da kasa sun nuna babban yabo ga bikin tunawa da ranar cika shekaru 70 da cimma nasarar yaki da mayakan Japan
2015-09-09 21:40:08 cri
Shugabannin kasa da kasa, da shugabannin kungiyoyin duniya da suka kawo ziyara nan birnin Beijing, domin halartar bikin tunawa da cika shekaru 70 da cimma nasarar yakin kin harin Japan, tare da kin ra'ayin nuna karfin tuwo na Fascist, sun bayyana wannan biki a matsayin wani muhimmin mataki wanda ya shaida burin jama'ar kasar Sin ga kasashen duniya na tabbatar da zaman lafiya. Kaza lika ya gabatar da sakon kasar Sin a bayyane, cewa Sin za ta kokarta wajen tabbatar da zaman lafiya da lumana a duniya.

Game da hakan, shugaban kasar Rasha Vladimir Putin, ya bayyana cewa jawabin da shugaba Xi ya gabatar na nuna cewa Sin za ta kokarta wajen aiwatar da manufar samun ci gaba cikin lumana, kuma Rasha ta jinjinawa wannan mataki.

A nasa bangare, shugaban kasar Afirka ta Kudu Jacob Zuma, ya fidda wata sanarwa dake cewa wannan biki ya nuna cewa, Sin za ta tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali tare da duk sauran kasashen duniya. A matsayin wata babbar kasa, Sin ta aiwatar da matakan tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya, ba kuma tare da kai hari kan sauran kasashen duniya ba.

Bugu da kari Jacob Zuma ya bayyana cewa, Sin ta taka muhimmiyar rawa wajen 'yantar da kasashen Afirka, tare da ba da taimako mai dimbin yawa. Ya ce akwai dankon zumunci tsakanin Sin da kasashen Afirka cikin dogon lokaci. Har wa yau a yanzu dangantaka tsakanin sassan biyu ta shiga wani sabon mataki, inda bangarorin biyu ke kokarin gudanar da hadin gwiwa tsakaninsu, domin sa kaimi ga raya masana'antu, da samar da manyan ababen jin dadin jama'a a kasashen Afirka.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China