in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen duniya sun nuna babban yabo ga muhimmin jawabin da shugaba Xi Jinping ya yi
2015-09-07 16:57:10 cri
A kwanan baya, a yayin da suke zantawa da wakilanmu, mutane da dama a kasashen waje sun ci gaba da tofa albarkacin bakinsu game da muhimmin jawabin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi a gun bikin tunawa da ranar cika shekaru 70 da cimma nasarar yaki da mayakan Japan, inda ya bayyana wa duniya cewa, jama'ar Sin suna darajanta zaman lafiya, kuma za su ci gaba da rike darasi daga tarihi, a kokarin tabbatar da zaman lafiya a duniya, tare da sa kaimi ga bunkasuwar kasa da kasa baki daya.

Wani masanin kasar Sin dake aiki a kwalejin nazari kan dangantakar kasashen duniya dake Nijeriya, ya bayyana cewa, Sin ba ta taba tsoma baki kan harkokin cikin gida na kasashen Afirka ba. A maimakon haka, ta kan ba da ainihin gudummawa bisa yanayin da ake ciki, domin sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arziki da kyautata rayuwar jama'a. Bugu da kari, Sin ta rika jaddada cewa, bunkasuwa za ta ba da tabbaci ga samun zaman lafiya, haka kuma tabbatar da zaman lafiya zai samar da yanayi mai kyau ga samun bunkasuwa. A sabili da haka, bunkasuwar Sin ta ba da gudummawa ga tabbatar da zaman lafiya a duniya, tare da kawo zarafi mai kyau ga kasashen Afirka a wannan fanni. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China