in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane kimanin dubu daya ne daga tawagogin kasashen waje za su halarci faretin tunawa da cika shekaru 70 da kawo karshen harin Japanawa
2015-08-25 15:00:45 cri
Mataimakin shugaban ofishin shirya faretin tunawa da cika shekaru 70 da kawo karshen harin Japanawa manjo janar Qu Rui ya bayyana a yau Talata cewa, yanzu haka tawagogin soja da na wakilai guda 17 daga kasashen waje wadanda suka hada da mutane kimanin dubu daya za su halarci bikin, sun riga sun shiga sansanin horar da faretin.

A taron manema labaran da ofishin watsa labaru na majalisar gudanarwar kasar Sin ya gudanar game da bikin faretin, Qu Rui ya yi bayani game da tawagogin soja da na wakilai da 'yan kallo daga kasashen waje da za su zo kasar Sin don halartar bikin.

Qu Rui ya kara da cewa, kasashen waje sun tura tawagogin soja ko wakilai ko 'yan kallo zuwa kasar Sin don halartar bikin faretin tunawa da nasarar yaki da masu ra'ayin nuna karfi a duniya, da neman shimfida zaman lafiya mai dorewa a duniya, da kuma gwada hadin gwiwa mai inganci dake tsakaninsu da sojojin kasar Sin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China