in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban hafsan sojojin Najeriya ya tsallake rijiya da baya daga harin Boko Haram
2015-08-24 10:37:42 cri

A ranar Asabar din da ta gabata ne wasu da ake zargin 'yan Boko Haram ne suka kai wa tawagar babban hafsan sojojin Najeriya, Laftanar Janar, Tukur Burutai hari a kauyen Faljari da ke tsakanin Mafa da Dikwa.

Wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar sojojin Najeriyar Kanar Sani Usman Kukasheka, ta ce an kai harin ne a kan wasu daga cikin sojojin da ke tawagar hafsan wadanda suka wuce gaba.

Sai dai kuma sanarwar, ta ce, maharan ba su ji da dadi ba a hannun sojojin a inda sojojin suka kashe 'yan kungiyar har mutane 10, suka kuma kama guda 5 a raye.

Sanarwar ta kara da cewa, soja daya ya rasa ransa a lokacin gumurzun, sannan wasu guda 4 sun jikkata.

A ranar Asabar din ne hafsan sojojin Laftanar Janar, Tukur Burutai ya ziyarci sansanonin rundunonin sojin da ke yaki da Boko Haram wadanda ke a garuruwan Mafa da Dikwa.

A makonnin baya ne dai shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ba da wa'adin watanni uku ga sojan kasar da su kawar da kungiyar Boko Haram daga kasar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China