in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
WHO ta samar da cibiyoyin kiwon lafiya ga 'yan gudun hijira a Sudan ta Kudu
2015-08-20 12:53:48 cri

Hukumar lafiya ta duniya wato WHO tare da mataimakanta ta ce, sun samar da cibiyoyin kula da lafiya ga dubban 'yan gudun hijira wadanda rikici ya raba su da matsugunansu a arewa maso gabashin Sudan ta Kudu.

A watan Fabrairun shekarar 2014 ne hukumar ta WHO ta ayyana irin mummunan yanayin da fannin kiwon lafiya ya shiga a Sudan ta Kudu, ta ce, yanayin kiwon lafiyar ya kai mataki na kuma shi ne mataki mafi girma dake bukatar daukin gagagawa.

Hukumar lafiya ta duniyar ta ce, a watan Augusta, a kalla mutane dubu 10 ne suka isa yankin Malakal, yankin dake zama garkuwa ga fararen hula bayan suka shafe tsawon wata guda suna kokarin kutsawa yankin, a yanzu haka yawan 'yan gudun hijirar dake zaune a yankin tare da iyalansu ya kai dubu 46 da 567, wadanda suke cikin mawuyacin hali na kamfar ruwan sha da rashin tsabtar muhalli.

A cewar babban jami'in sashen dake kula da barkewar cutuka a Sudan ta Kudu, Allan Mpairwe, yanzu haka yankin na Malakal ya zama matattarar dubban 'yan gudun hijirar al'ummar Sudan ta Kudu wadanda a kullum yawansu na karuwa, lamarin da ya haddasa gurbacewar ruwan sha da kuma yaduwar cutuka kamar su cutar gudawa da dangoginta da cutar hanta da dai sauransu. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China