in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Koriya ta Arewa ta ce ba za ta yi koyi da yarjejeniyar nukiliyar Iran ba
2015-07-22 14:03:14 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Koriya ta Arewa, ya ce kasarsa ba za ta yi koyi da yarjejeniyar da aka cimma game da batun nukiliyar kasar Iran a dukkan fannoni ba, wajen warware batun nukiliyar ta.

Jami'in ya ce Koriya ta Arewa ba ta fatan dakatar da raya makaman nukiliya ko yin watsi da tsarin ta game da hakan. Wannan ne karo na farko da gwamnatin kasar Koriya ta Arewa ta bayyana ra'ayinta game da batun nukiliyar kasar ta Iran.

Kakakin ya bayyana cewa, a kwanakin baya wani jami'in ma'aikatar harkokin wajen kasar Amurka, ya bayyana cewa idan Koriya ta Arewa ta nuna sahihiyar aniya ta kawar da makaman nukiliya, kasar Amurka za ta shirya shawarwari tare da kasar. Ya kuma yi fatan yarjejeniya game da batun nukiliyar Iran za ta ja hankalin Koriya ta Arewa ta sake yin la'akari da na ta batun nukiliyar.

Haka zalika kuma, kakakin ya jaddada cewa nuna karfi, ta hanyar mallakar makaman nukiliya ita ce manufar kasar Koriya ta Arewa, game da tinkarar manufar barazana, da nuna kiyayya daga kasar Amurka. Kana ya ce muddin dai Amurka za ta ci gaba da nunawa kasar Koriya ta Arewan kiyaya, to, manufar kasar game da mallakar makaman nukiliya ba za ta canza ba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China