in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jihar Xinjiang ta tabbatar da musulmai su yi azumi yadda ya kamata
2015-07-17 10:24:49 cri
Tun lokacin da aka fara azumin watan Ramadan, aka tabbatar da samar da kayayyaki a kasuwannin sassa daban daban na jihar Xinjiang ta kasar Sin, da binciken wuraren gudanar da harkokin addini a fannonin wutar lantarki, ruwa da kuma gine-gine, da kai ziyara musulumai, da kuma tabbatar da cewa, musulmai sun yi azumin yadda ya kamata.

A watan na azumi, wata girgizar kasa mai karfi maki 6.5 bisa ma'aunin Richter ta faru a garin Pishan dake kudancin jihar Xinjiang, wadda ta haddasa mutuwa da raunatar wasu mutane da lallata wasu gine-gine da masallatai 304. Hukumomin da abin ya shafa sun yi bincike kan yanayin masallatan, inda aka tsugunar da musulmai dubu 35 a wasu wurare na wucin gadi don su ci gaba da gudanar da harkokinsu na addini. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China