in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar wakilan jama'ar kasar Sin ta amince da samar da kudade ga bankin NDB
2015-07-01 19:40:13 cri
A ranar Larabar nan ne majalisar wakilan jama'ar kasar Sin, ta amince da yarjejeniyar samar da kudade ga bankin NDB, wanda aka amince da kafawa domin raya kasashe mambobin kungiyar BRICS da ma sauran kasashe masu tasowa.

Rahotanni sun bayyana cewa zaunannen kwamitin majalissar ne ya zartas da kudurin amincewa da hakan, yayin taron da yake gudanarwa a watanni biyu biyu.

An dai cimma yarjejeniyar samarwa bankin na NDB kudade ne a ranar 15 ga watan Yulin shekarar bara, a yayin taron kolin kungiyar ta BRICS, batun da ya samu amincewar daukacin kasashe 5 mambobin kungiyar, wato kasashen Brazil, da Russia, da India, da Sin da kuma Afirka ta Kudu.

A cewar ministan kudin kasar Sin Lou Jiwei, bankin zai taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa hadin gwiwa tsakanin kasashe mambobin BRICKS ta fannin hada-hadar kudi, tare da fadada samar da ababen more rayuwa, da wanzar da ci gaba tsakankanin kasashe masu tasowa.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China