in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Nigeriya zai je Kamaru don tattauna batun Boko Haram
2015-06-24 10:48:28 cri

Shugaban kasar Nigeriya Muhammadu Buhari zai je kasar Kamaru bayan kammala azumin watan Ramadan don tattaunawa da takwaransa Paul Biya game da batun yaki da ta'addanci.

Kamar yadda kakakin fadar shugaban kasar Femi Adesina ya bayyana a cikin wata sanarwa a ranar Talata, ziyarar ta zo ne sakamakon gayyatar da shugaba Biya ya aiko na bukatar su hadu a tattauna da sauran kasashe makwabta a kan yaki da ta'addanci.

Ministan mulkin yanki da daidaita kasa ta Kamaru, Sadi Rene Emmanuel ne ya kawo wa shugaba Buhari wasikar gayyatar.

Sanarwar ta ce, shugaba Buhari ya amince da halartar tattaunawar a kasar Kamaru, in an kammala azumin watan Ramadan. (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China