Aiwatar da aikin wata rundunar sojojin ajiya ta Afrika na kan hanya domin taimaka wajen fuskantar duk wasu matsalolin tsaro a nahiyar, in ji shugaban kasar Zimbabwe kuma shugaban kungiyar tarayyar kasashen Afirka AU a wannan karo, Robert Mugabe, a yayin bikin rufe taron kungiyar AU karo na 25 a birnin Johannesburg.
Mun amince da wata yarjejeniya kan wajabcin gaggauta kafa wata rundunar sojojin ajiya ta Afrika da za'a mu iya tura wa a yankunan Afrika daban daban dake fama da rikici. Kasashen Afrika sun kafa wasu tsare tsare domin ganin an cimma wannan burin, in ji Mugabe. (Maman Ada)