in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tawagar tsaro ta yankin gabashin Afirka na daf da soma aiki
2014-04-24 10:42:01 cri

Mai yiwuwa ne tawagar tsaron kota-kwana, ta kasashen gabashin Afirka za ta soma aiki gadan-gadan, nan da watan Disambar karshen shekarar nan.

Tawagar ta EASF wadda ake fatan za ta kunshi sojoji da 'yan sanda da kuma wasu fararen hula, za ta tallafawa kasashen yankin ne, wajen magance kalubalen ayyukan ta'addanci.

An dai bayyana bukatar fara amfani da wannan tawaga ne, yayin taron yini uku da ministocin tsaro, da sauran wakilan kungiyar tsaron kasashen gabashin Afirka suka gudanar a ranar Laraba.

A jawabinsa ga mahalarta taron, ministan tsaron kasar Rwanda James Kabarebe, ya ce, akwai kyakkyawan tsari na musamman da aka tanada, domin tabbatar da nasarar aikin tawagar. Hakan a cewar sa zai tabbatar da nasarar burin da ake da shi, na dakile yaduwar manyan laifuka, ciki hadda fashin teku, da farautar namun dajin da dokokin kasashen suka haramta.

Bugu da kari tawagar za ta ba da gudummawa ta musamman wajen magance rikice-rikice, da wanzar da zaman lafiya.

Taron wanda aka gudanar a birinin Kigali ya samu halartar wakilai daga kasashen Rwanda, da Uganda, da Kenya, da Burundi, da Kamaru. Sauran sun hada da Jibouti, da Habasha, da Seychelles, da Somaliya da kuma Sudan. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China