in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 11 suka hallaka a harin kunar bakin wake a arewa maso gabashin Nigeriya
2015-06-16 09:46:21 cri

Rahotanni daga Nigeriya sun tabbatar da cewa, a kalla mutane 11 ne suka hallaka a ranar Litinin din nan a wasu hare-haren kunar bakin wake guda biyu a garin Potiskum, kamar yadda wata majiyar asibiti ta tabbatar wa kamfanin dillancin labarum kasar Sin Xinhua.

Hare-haren dai ana zargin 'yan kungiyar Boko Haram guda biyu ne suka kai su, wani a kan ofishin 'yan tsaro na saka kai da aka kafa domin kare mazauna daga irin wadannan hare-hare, sannan saura daya kuma a wata mashaya, in ji wani likita da ya nemi a sakaya sunan shi.

A kalla dai kuma mutane 8 sun samu raunuka suna karban magani, in ji likitan.

Potiskum, garin kasuwanci mafi girma a jihar Yobe ya taba samun hare hare da dama baya. (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China