in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Najeriya zai kai ziyara a Chadi da Nijar domin tattauna matsalar Boko Haram
2015-06-03 10:40:23 cri

Sabon shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari, zai kai ziyara a ranakun Laraba da Alhamis a kasashen Nijar da Chadi a yayin da kungiyar Boko Haram ta sake fito da sunanta a cikin wani sabon bidiyonta.

Kakakin shugaban Najeriya, Garba Shehu, ya bayyana a cikin wata sanarwa a ranar Talata cewa, shugaba Buhari zai je kasashen Chadi da Nijar domin tattauna barazanar kungiyar Boko Haram.

Wannan ziyara ta kwanaki biyu za ta mai da hankali kan matsalar tsaro, in ji mista Shehu, tare da nuna cewa, Najeriya na bukatar taimakon kasashe makwabtanta domin cimma nasara kan kamfen da take yi na yaki da kungiyar Boko Haram wanda ayyukanta suka janyo asarar rayukan mutane fiye da dubu goma sha biyar tun daga shekarar 2009. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China