in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kenya na tattauna yiwuwar tsawaita layin dogo da kamfanin Sin ke ginawa a kasar
2015-05-28 09:57:08 cri

Mahukuntan kasar Kenya sun fara wata tattunawa da kamfanin kasar Sin wanda ke ginin layin dogo na zamani a kasar, da nufin duba yiwuwar tsawaita nisansa zuwa garin Naivasha dake arewa maso yammacin kasar.

Shugaba Uhuru Kenyatta ne ya bayyana hakan, jim kadan da kammala ziyararsa a wurin da ake gudanar da aikin a yankin Voi. Ya ce, idan har an cimma matsaya game da tsawaita layin dogon, za a kara kusan kilomita 120 bisa asalin kwangilar da aka daddale, ya zuwa rukunin masana'antu da za a gina a Naivasha, wurin da ake fata samar da wutar lantarki ta zafin kasa.

Wannan sabon layin dogo da za a gina a Kenya dai zai hade manyan biranen kasar, wato Nairobi zuwa Monbasa, shi ne kuma aiki irin sa mafi girma da ake gudanarwa a kasar, tun bayan samun 'yancin kai a shekarar 1964.

Kaza lika aikin zai hade Kenya da kasashen gabashin Afirka, kamar Tanzania, da Uganda, da Rwanda, da Burundi da kuma Sudan ta Kudu. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China