in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An rufe taron nazarin yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya
2015-05-23 16:36:20 cri
A jiya Jumma'a 22 ga wata, aka rufe taron nazarin yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya karo na 9 a hedkwatar MDD da ke birnin New York. A cikin tsawon makwanni hudu da ake gudanar da taron, kasashe 190 da suka daddale yarjejeniyar sun yi cikakken nazari a kan yadda aka aiwatar da ita, tare da tattauna matakan da za a dauka a gaba.

Sassa daban daban mahalarta taron sun yaba wa yarjejeniyar a kan yadda ta taimaka a kiyaye zaman lafiya da tsaro da kwanciyar hankali a duniya, sa'an nan sun bayyana goyon bayansu game da kwance damarar nukiliya da hana yaduwar makaman nukiliya da kuma yin amfani da makamashin nukiliya cikin lumana da aka tsara cikin yarjejeniyar, tare da inganta kwarjinin yarjejeniyar da kuma ingancinsa.

Sai dai sakamakon yadda wasu kasashe ke fama da babban sabanin ra'ayi a kan kafa yankin rashin kasancewar makaman nukiliya da sauran manyan makaman kare dangi a yankin gabas ta tsakiya, taron ya kasa cimma wata yarjejeniya a kan batun.

Tawagar wakilan kasar Sin ta halarci taron a karkashin jagorancin mataimakin ministan harkokin waje na kasar Mr.Li Baodong, wanda ya gabatar da jawabi a yayin babbar mahawarar taron. A yayin taron, tagawar kasar Sin ta bayyana matsayin kasar a kan wasu muhimman batutuwa.

A kan kira taron nazarin yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya a shekaru biyar biyar, kuma an fara taron na wannan karo a ranar 27 ga watan Afrilun da ya gabata.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China