in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya bukaci a kai zuciya nesa bayan yunkurin juyin mulki a Burundi
2015-05-14 09:52:36 cri

Babban magatakardar MDD Ban Ki-moon ya bukaci daukacin masu fada a ji a kasar Burundi, da su kai zuciya nesa bayan wani yunkuri na juyin mulkin soji, wanda a cewar fadar shugaban kasar bai yi nasara ba.

Da yake bayyana hakan, kakakin MDD Stephane Dujarric, ya ce, Ban Ki-moon na fatan daukacin sassan da wannan batu ya shafa za su dauki matakan samar da daidaito, da wanzar da zaman lafiya, duba da hali na rashin tabbas da kasar ta Burundi ke ciki a yanzu haka.

A ranar Laraba ne dai tsohon shugaban hukumar leken asirin kasar Burundi Manjo Janar Godefroid Niyombare, ya tabbatar da aukuwar wannan juyin mulki, wanda a cewarsa ya kawo karshen mulkin gwamnatin kasar mai ci, kuma tuni aka fara shirin kafa gwamnatin rikon kwarya. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China