in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Magatakardar MDD ya yaba da yadda aka tafiyar da babban zaben Togo cikin lumana
2015-04-27 15:42:21 cri

Babban magatakardar MDD Ban Ki-moon a ranar Lahadin nan ya yaba a kan yadda aka tafiyar da babban zaben a kasar Togo cikin lumana.

A ranar Asabar ne dai al'ummar kasar miliyan 3.5 wadanda suka cancanci kada kuri'an suka kada kuri'unsu a tashoshin zabe 8,994 a daukacin fadin kasar mai al'umma miliyan 6.2 wadda take yammacin Afrika.

Kakakin magatakaradar a cikin wata sanarwa da ya fitar ya ce, Mr Ban Ki-moon yana kira ga 'yan siyasa da sauran sassan daban daban na jama'ar kasar da su yi amfani da lokacin jiran sakamakon zaben su ci gaba da zama cikin kwanciyar hankali da lumana yadda ya kasance a lokacin zaben.

Haka kuma Mr Ban ya bukaci dukkan 'yan takara da magoya bayansu da su warware rashin fahimta dake tsakanin su ta hanyar zuwa ga hukumomin shari'a.(Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China