Tawagar tsohon shugaban tsibirin Madagascar Marc Ravalomanana ta dauki niyyar dakatar da halartarta a cikin shirin sassanta 'yan kasa. Mista Ihanta Randriamandranto, mamba na tawagar, ya bayyana a ranar Litinin cewa, bangaren Ravalomanana ya dauki niyyar janye jiki har sai mun samu karin haske kan sahihiyar manufar da ake baiwa batun sassanta 'yan kasa.
A cikin watan Febrairun da ya gabata, tsoffin shugabannin kasar Zafy Albert da Andry Rajoelina sun sanar da janyewarsu daga shirin sassanta 'yan kasa da kwamitin mabiya addinin kirista (FFKM) ke jagoranta. (Maman Ada)