in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za mu dauki karin matakai na magance matsalolin zabe, in ji INEC
2015-04-08 11:09:28 cri

Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta a Najeriya Farfesa Attahiru Jega, ya jaddada kudurin hukumarsa, na ci gaba da daukar karin matakan dakile duk wasu matsaloli da ka iya bullowa, yayin zaben gwamnoni, da na 'yan majalissun jihohin kasar da za a gudanar a ranar Asabar mai zuwa.

Farfesa Jega, ya bayyana hakan ne yayin da mambobin kwamitoci 2, na majalissar dokokin tarayyar kasar, wadanda suka sanya ido a zaben da ya gabata suka kai masa ziyara a ofishinsa. Ya kuma kara da cewa, INEC za ta kokarta wajen warware matsalolin da ta fuskanta, yayin zaben shugaban kasa da ya gabata a ranar 28 ga watan Maris. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China